Isa ga babban shafi
Amurka

Shirin hana baki daga kasashen musulmi biyar shiga Amurka ya tabbata

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana samun gagarumar nasara a shirinsa na hana baki daga kasashe biyar na musulmai zuwa kasar sakamakon wani hukuncin kotun koli da ya amince da matakin.

Donald Trump, shugaban Amurka
Donald Trump, shugaban Amurka 路透社。
Talla

Alkalai 5 suka kada kuri’ar goyan bayan shirin, yayin da 4 suka ki amincewa da shi, abin da ke tabbatar da nasarar Trump a wannan takun-saka da na tsawon watanni tsakanin shugaban da wadanda ke kallon matakin a matsayin wanda ya yi hannun riga da matsayin Amurka na kasa jagora a tattalin arziki da kuma siyasar duniya.

Wannan mataki zai shafi baki ‘yan kasashen Iran, Libya, Somalia, Syria da kuma Yemen, sai Koriya ta Arewa wadda shugaban ya sanya ta a cikin shirin.

Trump ya ce ya dauki mataki ne domin tabbatar da tsaron Amurka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.