Koriya ta Arewa za ta lalata tashar sarrafa nukiliyarta
Kasar Koriya ta Arewa na cigaba da nuna sassauci kan manufofin ta ganin yadda a karon farko ta baiwa Majalisar Dinkin Duniya damar shiga wasu Yankunan kasar.Isar tawagar Majalisar Koriya ta Arewa na jaddada kokarin hukumomin kasar na shiga matakin kulla huldar diflomasiya da manyan kasashen Duniya da dama wanda ke tabbatar da kawo karshen shirin sarrafa makamin nukiliya baki daya.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwar da shugaba Kim ya gabatar yau asabar ta bayyana cewar za’a lalata wurin gwajin makamin kasar tsakanin ranar 23 zuwa 25 ga watan nan.
A farkon wannan makon Shugaban Amurka Donald Trump da takwaran sa na Koriya ta Arewa Kim Jong Un suka tsaida ranar 12 ga watan Yuni a matsayin ranar da zasu gana a kasar Singapore.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu