Kotun Koli ta goyi bayan hana Musulmai shiga Amurka
Kotun kolin Amurka ta bai wa gwamnati damar fara aiki da kudurin dokar da ke hana wa ‘yan asalin wasu kasashe 6 na Musulmi damar shiga kasar kafin yanke hukunci dangane da karar da wasu jihohi suka daukaka a wannan batu.
Wallafawa ranar:
Matakin dai ya shafi kasashen Chadi da Syria da Yemen da Iran da Somalia da kuma Libya, wadanda Amurka ta bayyana a matsayin masu hatsari ga makomar tsaronta.
Alkalai bakwai daga cikin tara a kotun sun janye hukuncin da wata karamar kotu ta yanke na dakatar da gwamnatin Amurka daga aiwatar da dokar haramta wa kasashen na Musulmin shiga kasar.
Sai dai a wannan makon ne kotunan daukaka kara na tarayya da ke Francisco na California da Richmond na Virginia za su yi zaman sauraren korafi kan matakin da kotun kolin ta dauka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu