EU na shirin bude ofishin jakadancinta a Libya
Kungiyar Kasashen Turai na shirin bude ofishin Jakadancinta a Libya a wani yunkuri na nuna goyan baya ga gwamnatin da ke samun goyan bayan Majalisar Dinkin Duniya.
Wallafawa ranar:
Wani daftarin da ake saran shugabannin kungiyar su amince da shi a taron da za ayi a makon gobe, ya nuna cewar kungiyar na shirin bude ofishinta a Tripoli.
Yanzu haka kasar Italiya da ta yi wa Libya mulkin mallaka ce kawai ke da ofishin jakadanci a Tripoli daga cikin kasashen kungiyar 28.
Kungiyar Turai ta dauke ofishinta daga Tripoli zuwa Tunisia ne a tsakiyar shekarar 2014 sakamakon tsananin tashin hankalin da kasar ta yi fama da shi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu