Isa ga babban shafi
Iran

Iran na mutunta yarjejeniyar nukiliya ta 2015

Masu bincike na hukumar hana yaduwar makaman nukiliya a duniya, sun ce Iran ta mutunta dukkanin sharuddan da ke kunshe a yarjejeniyar nukiliyar da ta kulla da kasashen duniya a shekara ta 2015.

Jami'an hukumar hana bazuwar makaman nukiliya a duniya (IAEA)
Jami'an hukumar hana bazuwar makaman nukiliya a duniya (IAEA) KAZEM GHANE / IRNA / AFP
Talla

Rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar ya ce, binciken watanni hudu-hudu da aka saba gudanarwa, ya tabbatar da cewar har yanzu ba inda kasar ta saba wa sharuddan da aka gindaya mata.

 

Bayanan na IAEA ya zo ne a daidai lokacin da Amurka ke cewa akwai bukatar aikewa da masu bincike zuwa barikokin sojin Iran domin tabbatar da cewa ba ta gudanar da ayyukan nata na nukiliya a boye.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.