Najeriya ta bukaci janye hukuncin kisa kan 'yan kasar
Gwamnatin Najeriya ta roki Indonesia da ta yi wa Allah ta sauya hukuncin kisan da ta yanke wa 'yan Najeriya 50 zuwa daurin rai da rai.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ministan Harkokin Wajen Najeriya Geoffrey Onyeama ya gabatar da bukatar a ganawar da suka yi da takwararsa ta Indonesia Retno Marsudi.
Kungiyoyin kare hakkin Bil Adama sun bukaci gwamnatin Najeriya da ta kara kaimi wajen ganin an kubutar da 'yan kasar da ke jiran a aiwatar mu su da hukuncin kisan.
Kungiyar LEDAP ta ce, akalla 'yan Najeriya 300 ke jiran a aiwatar mu su da hukuncin kisa a kasashen Asia sakamakon samun su da laifin safarar miyagun kwayoyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu