Firaministan Isra'ila Netanyahu na Halartan Taron ECOWAS/CEDEAO a Liberia
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu na halartan taron shugabannin kungiyar Kasashen yammacin Africa ECOWAS ko CEDEAO da aka fara Lahadi a birnin Monrovia na Liberia.
Wallafawa ranar:
Ya fadi cewa Isra'ila na neman komawa nahiyar Africa sosai kuma ya gamsu da dimbin albarka dake cikin nahiyar.
A jawabinta wajen bude taro, Shugaban kungiyar mai barin gado kuma shugaban kasar Liberia Uwargida Ellen Johnson Sirleaf ta yabawa kungiyar saboda aikin da Dakarun Kasashen suka yi wajen maido da zaman lafiya a kasar Liberia.
Ta yi nuni da cewa ayyukan taddanci da ake samu yanzu na matukar shafar zaman lafiyar yankin kasashen.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu