Isa ga babban shafi
Ebola

Masana sun bayyana wasu hadduwan kamuwa da cutar Ebola

Masana harkokin kiwon lafiyar jama’a sun gano cewa mutanen da suka rayu bayan sun yi fama da cutar Ebola, na iya fuskantar matsaloli lafiyar jikin su nan gaba. 

Shugaban kungiyar Lafiya ta duniya Margret Chan
Shugaban kungiyar Lafiya ta duniya Margret Chan Reuters/路透社
Talla

Masanan na bayyana haka ne bayan sun gudanar da wasu gwaje-gwaje a kasar Guinea inda suka gano cewa ala tilas sai duk wanda ya taba kamuwa da cutar kuma ya warke sai ya cigaba da kai kansa wajen likitoci suna duba lafiyarsa.

Bayan gudanar da binciken masanan sun bayyana cewa kusan mutun daya daga cikin mutane 4 da suka taba kamuwa da wannan cuta har  suka warke an gano cewa suna fama da ciwon gabobi, yayinda kashi 35% na fama da ciwon kai, kashi 22% kuma na fama da ciwon ciki.

An tsara gudanar da binciken cutar Ebola ne a kasar Guinea na tsawon shekaru biyu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.