Isa ga babban shafi
Guinea

Cutar Ebola Ta Sake Kashe Mutun Daya A Kasar Guinea.

An sake samun wani mutun daya da ya mutu a kasar Guinea sakamakon cutar Ebola wadda ta sake bulla a kasar.  

Maaikacin Lafiya sanye da kayan kariya daga cutar Ebola a bakin aiki a kasar Guinea
Maaikacin Lafiya sanye da kayan kariya daga cutar Ebola a bakin aiki a kasar Guinea KENZO TRIBOUILLARD / AFP
Talla

A ranar Lahadi data gabata aka sami mutun na farko daya mutu sakamakon wannan cuta bayan anyi bankwana da ita tun cikin shekarar data gabata.

Wani mai Magana da yawun Hukumomin lafiya a kasar Guinea,  Ibrahima Sylla ya gaskata mutuwar mutun na biyu yau Talata.

Ya ce sun sami mutane takwas da suka mutu daga cikin mutane tara da suka kamu da wannan cuta.

A cewar sa mace ce ta gamu da ajalin ta a garin Nzerekore dake kan iyaka da kasar Liberia inda aka sami wasu da suka kamu da wannan cuta.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.