Isa ga babban shafi
Syria

MDD za ta binciki laifukan yaki a Syria

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shirin kafa wani kwamiti da zai tattara bayanan aikata laifukan yaki a Syria.

Yakin Syria ya hallaka mutane sama da dubu 300 a cikin shekau 5
Yakin Syria ya hallaka mutane sama da dubu 300 a cikin shekau 5 REUTERS/Omar Sanadiki
Talla

Wannan dai wani yunkuri ne na ganin an hukunta wadanda suka aikata laifuka a yakin kasar da aka kwashe kusan shekaru 6 ana gwabzawa.

Kudirin da Liechestein ta gabatar tare da kasashe 58, cikinsu  har da Amurka da Faransa da Birtaniya da Jamus da kuma Saudi Arabia, ya samu goyan bayan kasashe 105 a babban zauren Majalisar, yayin da 15 suka ki nuna goyon bayansu, in da kuma 52 suka ki kada kuri’a.

Ana saran kwamitin ya yi aiki da kwamitin binciken da aka kafa a baya wanda ya yi bayani kan yadda aka rika cin zarafin dan Adam a yakin da yanzu haka ya lakume rayukan mutane sama da 310,000.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.