Isa ga babban shafi
Haiti

Mamata Sakamakon Iska da Goguwa a Kasar Haiti Sun Haura 800

MDD ta yi gargadin cewa zai dauki lokaci kafin sanin takamaiman yawan mutanen da suka mutu sakamakon mummunar iska da ruwan sama mai karfi da ake kira Hurricane Mathew data ratsa kasar Haiti, da yazuwa yau Asabar  ake fadin cewa mutane 800 suka mutu.

Barna da iska da ruwan sama da ake kira Hurricane Mathew ta yi a Haiti
Barna da iska da ruwan sama da ake kira Hurricane Mathew ta yi a Haiti REUTERS/Carlos Garcia Rawlins
Talla

Kungiyar samar da abinci ta duniya ta ce wasu wurare da yawa an gaza isa dole sai ta jiragen sama ko jiragen ruwa.

Yawancin hasarar rayukan a Haiti sun auku ne a gaban tekun kudu maso yammacin kasar.

Igiyar ruwan da goguwa yanzu haka ta tunkari gaban tekun jihar Florida na Amurka duk da cewa ta rage karfin ta sosai, inda wayewar gari Asabar aka gano mutane 4 suka mutu.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.