Isa ga babban shafi
Iraqi

Mutane 213 ne suka mutu a harin ta'addanci a Bagadaza na Iraki

Jimi'llan mutane 213 aka karas da sun gamu da ajalinsu sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai birnin Bagadaza na kasar Iraqi ranar lahadi, wanda kungiyar IS ke ikirarin ita ta kai shi.

Barna da aka samu a harin Bam ranar lahadi
Barna da aka samu a harin Bam ranar lahadi REUTERS/Khalid
Talla

Jami’an Gwamnatin kasar suka gabatar da sabbin alkaluman mamatan a yau littini a birnin Bagadaza.

Harin na kunar bakin wake, cikin wata mota da aka shake ta da bama-bamai an kaishi ne a wani yanki da jama’a ke taruwa, da gine-gine da shaguna masu yawa.

Jimi'llan mutane 200 suka jikkata kamar yadda jami'an tsaro da majiyoyi a asibiti suka shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa AFP.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.