Isa ga babban shafi
Colombia

Colombia ta sasanta da ‘Yan tawayen FARC

Gwamnatin Kasar Colombia ta sanar da kulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta din-din-din tsakaninta da ‘Yan Tawayen FARC domin kawo karshen yakin basasan da aka kwashe shekaru 50 ana yi a kasar.

'Yan tawayen FARC sun jima suna yaki da dakarun Colombia
'Yan tawayen FARC sun jima suna yaki da dakarun Colombia LUIS ROBAYO / AFP
Talla

A sanarwar da bangarorin biyu suka rabawa manema labarai sun ce sun yi nasarar kulla yarjejeniyar kawo karshen duk wani tashin hankali a kasar.

Ana sa ran yau Alhamis shugaban kasa Juan Manuel Carlos da kwamandan ‘Yan Tawayen Timoleon Jimenez za su bayyana nasarar da aka samu a wani biki da wasu shugabannin kasashen duniya da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya za su halarta.

Tun a 1960 Colombia ke rikici da ‘Yan tawayen FARC, wanda ya salwantar da rayukan mutane sama da dubu dari da hamsim tare da raba sama da mutane Miliyan bakwai da gidajensu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.