Isa ga babban shafi
Syria

MDD za ta sake zaman sasanta rikicin Syria

Jakaadan majalisar dinkin duniya kan sasanta rikicin Syria, Staffan de Mistura ya ce, zai sake gudanar da wani taron zaman lafiya a watan gobe bayan ya bukaci tsagaita wuta sakamakon sabon tahin hankalin da aka samu wanda ya hallaka fararen hula sama da 20 a birnin Aleppo.

Manzan musamman na majalisar dinkin duniya a Syria Staffan de Mistura
Manzan musamman na majalisar dinkin duniya a Syria Staffan de Mistura REUTERS/Denis Balibouse
Talla

De Mistura ya bukaci kasashen Amurka da Rasha da su gaggauta tsoma baki a matakin kololuwa domin ceto tattaunawar zaman lafiyar kasar ta Syria.

A lokacin da ya ke yi wa manema labarai jawabi bayan ya gana da kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya, Mr. De Mistura ya ce, yarjejeniyar da aka cimma a watan Fabarairu na cikin wani hali.

Wata kungiyar sa- kai doimin kare fararen hula, White Helmets ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa, kananan yara na cikin wadanda suka mutu a sabon tashin hankalin wanda aka samu a jiya Laraba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.