Isa ga babban shafi
Burundi

Komitin Sulhu na MDD ya Umarci tura 'Yan Sanda Burundi

Komitin Sulhu na MDD ya umarci Babban Sakatare Janar na Majalisar Ban Kimoon da ya gaggauta tura ‘yan sanda zuwa kasar Burundi, inda ake fargaban kazancewa rikicin kabilanci a fadin kasar. 

Shugaban Burundi Pierre Nkurunziza tare da Babban Sakatare Janar na MDD Ban Ki-moon a wajen wani taro a Bujumbura a watan biyu na shekara ta 2016
Shugaban Burundi Pierre Nkurunziza tare da Babban Sakatare Janar na MDD Ban Ki-moon a wajen wani taro a Bujumbura a watan biyu na shekara ta 2016 STRINGER / AFP
Talla

Shekara daya kenan ake samun kashe-kashen mutane a kasar tun lokacin da Shugaban kasar Pierre Nkurunziza ya kafe da sai ya zarce da mulki bayan cikan waadin mulkin sa kamar yadda kundin tsarin mulki ya nema.

Rayukan mutane 439 suka salwanta ya zuwa yanzu, yayinda wasu mutane dubu 250 aka tilasta masu tserewa daga gidajensu.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.