Isa ga babban shafi
Denmark

Cutar Zika ta shiga Denmark

Hukumomin kiwon lafiya a kasar Denmark sun ce yanzu haka an kwantar da mutun na farko da ake zargin cewa yana dauke da kwayar cutar Zika, wadda ke ci gaba da yaduwa a cikin kasashen Latin Amurka.

Kwayar cutar zika da sauro ke yadawa ta hanyar cizo
Kwayar cutar zika da sauro ke yadawa ta hanyar cizo REUTERS/CDC/Cynthia Goldsmith/Handout
Talla

An dai kwantar da mutumin ne da aka ce bai jima da dawowa daga wata kasa ta kudancin Amurka ba, inda ake fargabar ya kamu da wannan cuta ta Zika, wadda ke sa ana haifar yara da kananan kawuna.

Ita ma Birtaniya ta ce, matafiyanta da ke dawowa daga yankin kudancin Amurka, sun shigo da cutar yayin da kasar Netherlands ta tabbatar cewa 'yan kasarta 10 na dauke da cutar bayan sun dawo daga yankin kudancin Amurka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.