Isa ga babban shafi
Faransa

Jirgin Air France ya yi saukar gaggawa a Kenya

Jirgin Faransa na air France ya yi saukar gaggawa a kasar Kenya bayan samun wani kunshi da ake zargin Bom ne a cikin jirgin da ke kan hanyarsa daga Mauritius zuwa Paris.

jirgin Air France
jirgin Air France AFP
Talla

Jirgin ya bar Mauricius ne a jiya da dare dauke da fasinja 459, zuwa misalin karfe 1 na dare kuma ya yi saukar gaggawa a filin jirgin Moi a Mombasa kasar Kenya.

Rahotanni sun ce jami’an kwance bom da sojojin sama sun dauki kunshin domin tantance ko bom ne.

Har yanzu rahotanni sun ce jirgin yana kasar Kenya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.