Isa ga babban shafi
SYRIA

'Yan gudun hijra: EU za ta bai wa Jordan tallafi

Kungiyar tarayyar Turai ta bayyana cewa za ta bai wa kasar Jordan tallafin Euro miliyan 28 domin kula da ‘Yan gudun hijirar Syria da ke samun mafaka a kasar. 

Wasu daga cikin 'Yan gudun hijira
Wasu daga cikin 'Yan gudun hijira REUTERS/Stoyan Nenov
Talla

Kwamishinan kula da jin dadin jama’a na kungiyar ne Christos Stylianides ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyara a sansanin Zaatari da ke yankin Arewacin Jordan, inda ‘yan gudun hijira dubu 80 ke samun mafaka.

Ana sa ran za a yi amfani da wadannan kudaden wajan kula da lafiyar ‘yan gudun hijirar da kuma samar musu da tsaftataccen ruwan sha har ma da ba su ilimi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.