Isa ga babban shafi
Colombia

Colombia za ta kaddamar da hari akan ‘Yan tawayen FARC

Shugaban Kasar Colombia Juan Manuel Santos ya bai wa sojojin kasar umurnin kaddamar da sabbin hare hare kan ‘Yan Tawayen FARC bayan sun kashe sojoji 10 a wani harin kwantar baunar da suka kai mu su. A jawabin da ya yi wa al’ummar kasar ta talabijin shugaba Santos ya ce za a ci gaba da kai hare haren har illa masha Allahu.

Shugabana kasar Colombia, Juan Manuel dos Santos
Shugabana kasar Colombia, Juan Manuel dos Santos ©Reuters.
Talla

A baya dai an dakatar da fafatawar ne na wata guda bayan da ‘yan Tawayen suka amince da tsagaita wuta a shirin zaman lafiyar kasar a Havana.

‘Yan tawayen sun kai harin ne a yammacin Colombia kuma shi ne hari mafi muni da aka kai bayan kaddamar da shirin amincewa da yarjejeniyar zaman lafiya a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.