Isa ga babban shafi

Faransa tace ba gudu ba ja da baya a yaki da ta'addanci

Shugaban Faransa Francois Hollande yace ba gudu ba ja da baya, wajen yaki da ayyukan ta’addanci. Shugaban ya fadi hakan ne a gaban majalisar dokokin Canada, a lokacin daya kai ziyara a kasar.Shugaba Hollande dake jawabi a gaban majalisar dokokin kasar ta Canada, inda wani dan bindiga ya kai wa hari kusan makonni 2 da suka gabata, yace gamaiyyar kasashen duniya ba zasu yi kasa a gwiwa ba, a yakin da suke yi da ayyukan ta’adanci.Mr. Hollande yace ta’addanci na barazana ga ginshikin da aka kafa kasashen Faransa da Canada a kai, don haka a cewar shugaban, dole a tashi tsaye.Ya kuma yi bayani kan yadda kasashen 2 suka bi sawun sauran kasashen duniya dake ci gaba da kai hare ta sama kan mayakan kungiyar IS a Iraai, inda yace suna aiki tare don sauke nauyin da aka dora musu.A ranar 22 ga watan Oktoban daya gabata, wani dan bindiga ya kai hari a majalisar dokokin kasar ta Canada, dake birnin Ottawa, inda ya harbi wani soja dake gandi a kusa da ginin, kafin daga bisani ‘yan sanda suka bindige maharin. 

Shugaban Faransa François Hollande, lokacin da ya kai ziyara kasar Canada
Shugaban Faransa François Hollande, lokacin da ya kai ziyara kasar Canada REUTERS/Mike Sturk
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.