Isa ga babban shafi
Philippines

Gwamnatin Philippines ta cim ma yarjejeniya da Kungiyar Musulmi

Gwamnatin kasar Philippine ta cim ma yarjejeniyar zaman lafiya tsakaninta da shugabannin Kungiyar Musulmi ta Moro a yau Alhamis, wadanda ke tawaye da ita a wani mataki da zai kawo karshen rikicin yankin kudancin kasar da ya lakume rayukan dubban mutane.

Mayakan Moro a ksar Phillippines
Mayakan Moro a ksar Phillippines AFP PHOTO / TED ALJIBE / FILES
Talla

A Fadar Shugaban kasa ne bangarorin biyu suka sa hannu ga yarjejeniyar sulhu a fadar  a Manila.

Addinin Musulmi ya shiga kasar Philippines ne tun a wajajen karni na 13 saboda cudanyar kasuwanci da Larabawa.

Kungiyar ‘Yan tawayen Moro suna da mabiya sama da 10,000 masu dauke da makamai a cewar rundunar Sojin kasar Philliphines, kuma sun dade suna fafutikar kafa kasa mai cin gashin kanta a kudancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.