Syria
Amirka Ta Ce Syria Na Amfani da Makami Mai Guba
Hukumar Leken Asiri ta kasar Amurka wato CIA, ta ce a halin yanzu tana da cikakkun hujjojin da ke tabbatar da cewa an yi amfani da makamai masu guba a yakin kasar Syria. A taron manema labaran da ya gabatar a cikin daren jiya, kakakin fadar shugaban Amurka, Ben Rhodes, ya ce akalla mutane 100 zuwa 150 ne suka rasa rayukansu sakamakon yin amfani da wadannan makamai a kasar ta Syria.Mai magana da yawun fadar ta White House, ya ce bangaren shugaba Bashar Assad na da hannun wajen yin amfani da wadannan makamai.
Wallafawa ranar: