Thailand
An Fara Neman Hanyoyin Karshen Rikicin Siyasa
Masu zanga zangar kasar Thailand dake sanye da jajayen kaya, tare da gwamnatin kasar sun fara tattaunawa domin kawo karshen rikicin siyasar kasar a matakin farko.Prime Minista Abhisit Vejjajiva da ke makale cikin barikin sojan fiye da wata guda da ya gabata, ya ce yana shirye da neman hanyoyin kawo karshen rikicin da siyasar kasar, inda masu zanga zangar ke neman kiran sabon zabe tare da rushe majalisar dokoki.Kwashe tsawon lokaci ana zanga zanga a Bangkok babban birnin kasar ta Thailand, ya katsewar harkokin yau da kullum.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: