Isa ga babban shafi
Yemen-Huthi

Farmakin 'yan tawayen Huthi kan masallaci ya hallaka mutane 22 a Marib

Akalla mutane 22 sun mutu a farmakin 'yan tawayen Huthi na Yemen da suka harba makami mai linzami kan wani masallaci da ke kudancin birnin Marib a kasar.

Wasu mayakan 'yan tawayen Huthi na Yemen a yankin Marib.
Wasu mayakan 'yan tawayen Huthi na Yemen a yankin Marib. Mohammed Huwais AFP
Talla

Alkaluman dakarun Sojin da ke samun goyon bayan gwamnatin kasar ya nuna yadda farmakin ya hallaka fararen hula 22 tare da jikka wasu 19 ciki har da kananan yara.

Bayanai sun ce cikin daren jiya ne mayakan na huthi suka farmaki masallacin wanda ke yankin Al-Jawba matsayin martini kan hare-haren da sojoji masu samun goyon bayan kassahen larabawa ke kai musu.

Dubunnan mayakan na Huthi suka rasa rayukansu a ‘yan kwanakin nan sakamakon yadda dakarun larabawa karkashin jagorancin Saudiyya ke ci gaba da tsananta hare-hare kansu.

Wasu alkaluma da ma’aikatar yada labarai ta Yemen ta wallafa a shafinta na Twitter ta ruwaito ministan labarai  Moammar al-Eryani na cewa mutane 29 suka rasa rayukansu a farmakin kan masallaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.