Isa ga babban shafi
Afghanistan - Taliban

Mata za su yi karatun jami'a bisa sharadin rashin cakuda da maza - Taliban

Sabon ministan ilimi mai zurfin gwamnatin Taliban Abdul Baqi Haqqani ya ce za a bai wa matan Afghanistan damar shiga jami'o’i amma bisa sharadin ba za su cakudu da maza ba.

Wasu mata yayin zanga-zangar neman kare 'yancin su a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan.
Wasu mata yayin zanga-zangar neman kare 'yancin su a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan. AP - Wali Sabawoon
Talla

Haqqani ya ce tsarin ilimin Afghanistan ya canza sosai tun bayan zangon farko na mulkin kungiyar Taliban, lokacin da aka hana mata zuwa makarantu da jami'o'i.

A farkon wannan wata kungiyar Taliban ta sanar da cewa mata na da damar karatu a jami'a idan suka kiyaye sharadin sanya rigar abaya da nikabi.

Kungiyar Taliban dai tayi ikirarin nisanta kan ta da tsauraran manufofin da ta runguma  a zamanin mulkin ta na farko fiye da shekaru 20 da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.