Isa ga babban shafi

Donald Trump ya cacaki China a taron MDD

Shugaban Amurka Donald Trump ya cacaki China a taron Majalisar Dinkin Duniya inda ya zarge ta da yadawa duniya annobar korona wadda yanzu haka ta lakume rayukan mutane kusan miliyan guda.

Shugaban Amurka Donald Trump.
Shugaban Amurka Donald Trump. MANDEL NGAN / AFP
Talla

Shugaba Donald Trump yace ya zama dole China ta dauki alhakin yada cutar korona a duniya.

Tuni kasar China ta maida martani wajen zargi shugaba Donald Trump da yada annobar siyasa a taron Majalisar Dinkin Duniya, jim kadan bayan ya cacaki kasar a jawabin da ya gabatar.

Jakadan China a Majalisar, Zhang Jun, yace a daidai lokacin da kasashen duniya suka mayar da hankali wajen yaki da annobar COVID-19, kasar Amurka ta mayar da hankali ne wajen yada cutar siyasa.

Jakadan yace ya zama dole ya jaddada cewar, surutun da Amurka keyi a Majalisar bashi da tasiri dangane da taron dake gudana yanzu haka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.