Isa ga babban shafi
Turkiya

Majalisar Turkiya ta amince da karawa Erdogan karfin iko

Majalisar kasar Turkiya ta goyi bayan wani kuduri da zai karawa shugaban kasar Recep Tayyib Erdogan karfin iko.

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyib Erdogan
Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyib Erdogan REUTERS/Brendan McDermid
Talla

Kudurin ya samu goyon bayan ‘yan majalisu 339 yayinda 142 suka kada kuri’ar adawa da kudurin.

Idan har kudurin ya samu amincewar al’ummar kasar ta Turkiya a kuri’ar jin ra’ayi da zasu kada, a karo na farko za’a samar da shugaba mai cikakken iko a kasar tare da soke mukamin Firaminista a karo na farko a tarihin Turkiya.

Zalika karkashin kudurin za’a rika gudanar da zaben Majalisar kasar da na shugaban kasa a lokaci guda, wanda ake sa ran tsaida ranar 3 ga watan Nuwamban 2019 a matsayin ranar gudanar da zaben.

Ana sa ran kada kuria’ar jin ra’ayin jama’ar a watan Afrilu mai zuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.