An kwashe fararen hula dubu 25 a Aleppo
Kungiyar bayar da agajin gaggawa ta kasa da kasa Red Cross ta bayyana cewa, akalla mutane dubu 25 ne suka fice daga birnin Alepo na Syria tun bayan da aka fara kwashe fararen hula a makon jiya.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yawun kungiyar Ingy Sedky ta ce, a jiya Litinin kadai, sun kwashe mutane dubu 15 a gabashin birnin na Aleppo .
Jami’ar ta kara da cewa, a halin yanzu, dubban jama’a na ci gaba da dakon kwashe su a motocin safa.
Tun bayan da aka cimma yarjejeniyar kwashewar, kungiyar bada agajin ke sanya ido kan yarjejeniyar wadda Rasha da Turkiya suka amince da ita.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu