Fararen hula na dakon a kwashe su daga Aleppo
Dubban fararen hula da ‘yan tawaye na ci gaba da dakon kwashe su daga birnin Aleppo bayan gwamnatin Syria ta dakatar da aikin kwashe jama’a.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wani dan tawaye ya shaida wa kamafnin dillanmcin labaran Faransa na AFP cewa, an cimma sabuwar yarjejeniya don kwashe karin mutane daga birnin, amma gwamnatin kasar ba ta bada tabbaci kan sabuwar yarjejeniyar ba.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da shugaban Amurka Barack Obama ya nuna damuwarsa matuka kan rikcin Syria da ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da dubu 300.
Akalla mutane dubu 6 ne aka kwashe daga birnin a ranar Alhamis amma aka dakatar da aikin kwashewar a ranar Jumma'a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu