Isa ga babban shafi
Syria

Jiragen yakin Syria sun kai hare-hare sama da 150 cikin awwani 24

Mazauna birnin Aleppo sun ce jiragen yakin Syria sun kaddamar da sabbin hare-hare sama da 150 cikin awanni ashirin da hudu da suka gabata, hakan kuma yayi sanadin rasa rayukan sama da mutane 90 a arewacin birinin.

Wasu mazauna birnin Aleppo sun ceto kananan yara daga karkashin baraguzan gine gine da suka rushe
Wasu mazauna birnin Aleppo sun ceto kananan yara daga karkashin baraguzan gine gine da suka rushe AMEER ALHALBI / AFP
Talla

Hare-haren da aka kaddamar a yau Juma’a, bangare ne na sabon yunkurin da gwamnatin Syria ta kaddamar, domin kwace yankunan da ke karkashin ikon ‘yan tawaye a birnin Aleppo.

Harin yayi sanadin lalata kayayyakin bada agajin gaggawa da ke yankin tare da lalata wuraren karkashin kasa da fararen hula suke amfani da su wajen fakewa hare-haren bam.

Rahotanni sun ce, cigaba da luguden wutar a birnin Aleppo yana dakile kokarin jami’an bada agaji, na ceto fararen hula da sabon fadan ya ritsa da su.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.