Isa ga babban shafi
Syria

Rasha ta amince ta dakatar da kai hari Aleppo

Kasar Rasha ta ce a shirye ta ke, ta dakatar da luguden wuta kan ‘yan tawaye a Aleppo na Syria har na tsawon sa’o’i Arba’in da takwas kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta bukata.

Mutanen Aleppo na bukatar agajin abinci
Mutanen Aleppo na bukatar agajin abinci REUTERS
Talla

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaron Rashan Igor Konashenkov ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce Rasha ta yanke shawarar saboda ba masu kai kayan agaji damar isa ga fararen hula da fada ya ritsa da su a Aleppo.

Sai dai Rasha ta ce tana jiran bayani daga Majalisar Dinkin Duniya kan kammala shirin jami’an kai agajin, kafin daga bisani a sanar da ranaku da kuma lokutan da tsagaita wutar zata fara aiki.

A cewar ma’aikatar tsaron Rasha za a tabbatar da tsaron jami’an Majalisar Dinkin Duniyar yayin gudanar da ayyukansu na agaji.

Satin da ya gabata ne kasar Rasha ta yi tayin tsagaita wuta na tsawon sa’o’i uku a Aleppo tayin da Majalisar Dinkin Duniya ta ki amincewa da shi, a cewarta lokacin ba zai isa a kai agaji ga sama da mutane miliyan daya da rabi ba da ke matukar bugatar agaji.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.