Isa ga babban shafi
Syria

Yankunan da ke fama da yunwa a Syria za su fara samun tallafi

Ana sa ran isar da tallafi zuwa garuruwa uku da ke fama da yunwa a kasar Syria bayan sun kwashe watanni shida ba tare da samun abinci ba sakamakon kawanyar da sojoji suka mu su.

Mutanen Madaya na cikin mawuyacin hali a Syria
Mutanen Madaya na cikin mawuyacin hali a Syria Reuters/ MIDEAST-CRISIS/SYRIA-TOWN
Talla

Garuruwan sun hada da Madaya da Fuaa da Kafraya.

Mai Magana da yawun Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya Idlin Etefa Abeer ya ce yanzu haka motocin agaji na shirin tafiya garuruwan da aka yi wa kawanya .

A cewar shi yanzu haka an loda kayan abincin a cikin motocin wanda zai kai ga mutane 40,000 da ke Madaya da wasu mutane 20,000 da ke sauran garuruwan biyu.

Ya ce suna fatar cewar gobe kayan abincin za su isa garuruwan, kuma sun tattauna da bangarorin da abin ya shafa don tabbatar da cewar kayan abincin sun isa gare su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.