Isa ga babban shafi
Syria

Al Nusra ta yi watsi da matakin ‘Yan adawar Syria

Kungiyar al Nusra mai alaka da Mayakan Al Qaeda ta yi watsi da bukatun kungiyoyin ‘Yan tawayen Syria da suka amince a Saudiya su hau teburin tattaunawa da shugaban kasar Bashar al Assad.

Mayakan  al-Nusra, masu alaka da Al Qaeda
Mayakan al-Nusra, masu alaka da Al Qaeda AFP PHOTO/ZAC BAILLIE
Talla

Shugaban kungiyar ta Al Nusra Abu Muhammed Al Jolani ne ya yi watsi matakin wanda ya danganta a matsayin tarko tare da zargin ‘Yan adawar da laifin cin amanar kasa.

Wannan dai na zuwa a yayin da sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry zai nufi Moscow domin tattaunawa da mahukuntan Rasha kan batun shawo kan rikicin Syria.

A ranar Alhamis ne kungiyoyin ‘Yan adawar Syria suka amince su hada kai domin tunkarar Shugaba Bashar Assad a teburin tattaunawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.