Isa ga babban shafi
Syria

'Yan adawar Syria za su tattauna da gwamnatin kasar

Kungiyoyin ‘yan adawar Syria sun amince da zaman tattaunawa da gwamnatin shugaba Bahsar al-Assad, sai dai sun dage kan matsayinsu cewa dole Assad ya mika mulki ga gwamnatin rikwan kwarya domin gudanar da sabon zabe a kasar.

Zauren taron da aka gudanar a birnin Riyadh na Saudiya domin sasanta rikicin Syria.
Zauren taron da aka gudanar a birnin Riyadh na Saudiya domin sasanta rikicin Syria. KARIM ABOUMERI / AFP
Talla

Bayan kammala taro irinsa na farko da Saudiya ta jagoranta kan sulhunta rikicin Syria da ‘yan adawar kasar, dukkanin bangarorin siyasar kasar da ke adawa da shugabancin Bashar al-assad sun yi na’am da zaman tattaunawar, sai dai suna kan bakarsu na ya sauka daga mulki.

Rahotanni sun ce, yayin wannan zaman akwai daya daga cikin kungiyon 'yan tawayen kasar, Ahrar al-Sham da ta fice daga zauran taron, yayin da wasu majiyoyi ke cewa ita ma ta sanya hannu kan wannan yarjejniya na zama da gwamantin Assad domin samo bakin zaren warware rikicin Syria.

Jami’an diflomasiyar kasashe 17 ne suka halarci wannan taro da nufin kawo karshen yakin Syria da ke nema shiga shekara ta 5.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.