Kurdawan PKK sun umarci 'ya'yan Kungiyar su fice daga Iraqi
Shugabannin kungiyar Kurdawa PKK a Iraqi, sun bukaci ficewar mayakansu daga yankuna kurdawa da ke kasar, domin kare rayukan fararan hula da hare-hare sama da Turkiya ke kaiwa ke hallakawa.
Wallafawa ranar:
A wata sanarwa da suka fitar ofishin shugaban kurdawa yankin Massud Barzani ya ce bai kyautu fararran hula suke rasa rayukansu ba saboda su.
Wannan dai na zuwa ne a dai-dai loakcin da rahotannin ke cewa Sama da mayakan Kurdawa 260 ne suka rasa rayukansu a mako guda na jerin hare-haren da Turkiya Ke kaiwa kan mayakan a arewacin iraqi, yayin da ake samu asaran rayukan fararran hula da dama.
Turkiya dai ta lashi takobin kawar da ayyukan ta'addanci da ke neman zama barazana a kasarta, lamarin da ya sa kasar daukan matakin kaddamar da hare-haren sama a Iraqi da Syria kan mayakan ISIL da na Kurdawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu