Isa ga babban shafi
Pakistan

‘Yan bindiga sun kashe mabiya Shi’a 43 a Pakistan

Wasu ‘Yan bindiga sun bude wa wata mota kirar Bus wuta da ke dauke da mabiya Shi’a tare da kashe mutane akalla 43 da raunana 13 a birnin Karachi na kasar Pakistan a yau Laraba. ‘Yan bindiga guda shida ne suka bude wa Motar wuta da karamar Bindiga bayan sun zo saman babura, kamar yadda ‘Yan sandan Pakistan suka tabbatar.

Mutane sun yi cincirindo a harabar Asibitin Karachi bayan harin da 'Yan bindiga suka kai inda suka kashe akalla mutane 43 a Pakistan
Mutane sun yi cincirindo a harabar Asibitin Karachi bayan harin da 'Yan bindiga suka kai inda suka kashe akalla mutane 43 a Pakistan REUTERS/Akhtar Soomro
Talla

An bayyana harin a matsayin mafi muni tun harin da aka kai a watan Janairu inda wani dan kunar bakin wake ya dala wa kansa Bom a wani masallaci da ke kudancin Shikapur tare da kashe mutane 61.

Pakistan dai na fama da matsalar rikicin babbancin akida, musamman akan mabiya shi’a tsiraru a kasar mai yawan musulmi Miliyan 200.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.