Pakistan-India
Kasashen duniya suna fushi da Pakistan akan sakin maharin Mumbai
Kasashen India da Amurka da Faransa sun bayyana bacin ransu kan matakin da Pakistan ta dauka na sakin mutumin da aka zarga da laifin kitsa harin Mumbai a shekarar 2008 Zaki ur Rahman Lakhvi, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 166.
Wallafawa ranar:
Talla
Firaministan India, Narendra Modi da shugaban Faransa Francois Hollande da kuma mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka Jeff Rathke duk sun yi Allah wadai da matakin.
A ranar Alhamis ne mahukuntan Pakistan suka bayar da belin Lakhvi, kuma yana da damar yin walwala.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu