Isa ga babban shafi
Thailand

Sojoji sun karbe gwamnati a Thailand

Babban Kwamandan rundunar Sojin kasar Thailand Prayut Chan-O-Cha ya bayar da sanarwar karbe gwamnati a kafar Telebijin din kasar bayan kwashe watanni Thailand na cikin rudanin siyasa. Kwamandan na Soji ya yace sun karbe mulki ne domin daidaita al’amurra a kasar.

Sojojin Thailand sun karbe ikon tafiyar da al'amurra saboda rikicin siyasa
Sojojin Thailand sun karbe ikon tafiyar da al'amurra saboda rikicin siyasa Reuters
Talla

Akwai ganawa da Shugaban rundunar sojan kasar ya gudanar tare da shugabannin ‘yan siyasar kasar da ba sa ga maciji da juna, Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara amfani da wata dokar soja, da nufin hana barkewar tashe tashen hankula a kasar.

Rikicin siyasan kasar ta Thailand na afkuwa ne tsakanin gidan sarautar Bangkok da masu goya musu baya a bangare daya, da iyalan tsohon Firaminista Thaksin Shinawatra, attajirai da ke matukan samun goyon bayan al’ummar arewacin kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.