Isa ga babban shafi
Thailand

Kwamandan Soja ya gana da ‘Yan siyasa a Thailand

Shugaban rundunar sojan kasar Thailand ya jagoranci wani taro, da shugabannin ‘yan siyasar kasar da basa ga maciji da juna. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara afni da wata dokar soja, da nufin hana barkewar tashe tashen hankula a kasar.

Manyan hafsoshin Sojan kasar Thailand
Manyan hafsoshin Sojan kasar Thailand Reuters
Talla

An shafe fiye da sa’oi biyu ana gudanar da taron, kuma ya sami halartar bangarorin da ke hamayya da juna, tare da manyan jami’an gwamnatin kasar.

Taron da aka yi a birnin Bangkok, karkashin jagorancin kwamandan sojan kasar, Prayut ya gudana ne cikin tsauraran matakan tsaro, da wani mai goyon bayan zababbiyar gwamnatin kasar ya bayyana da yanayi mai inganci.

Rashin cimma matsaya a taron na jiya Laraba, yasa aka yanke shawarar ci gaba da zaman a yau Alhamis.

Rikicin siyasan kasar ta Thailand na afkuwa ne tsakanin gidan sarautar Bangkok da masu goya musu baya a bangare daya, da iyalan tsohon Firaminista Thaksin Shinawatra, attajirai da ke matukan samun goyon bayan al’ummar arewacin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.