‘Yan bindiga sun bude wuta a sansanin 'Yan adawa a Thailand
A kasar Thailand, wasu mutane dauke da makamai sun kai hari akan wani sansani da ‘yan adawa suka kafa a birnin Bangkok inda suka buda wuta tare da raunata mutane da dama a cikin daren Juma’a.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Hukumomin tsaro a birnin sun tabbatar da faruwar wannan lamari, da ke zuwa a daidai lokacin da masu adawa da Firaminista Yingluck Shiniwatra suka kuduri aniyyar kaddamar da wani gagarumin bore domin kawo karshen gwamnatinta a ranar litinin mai zuwa.
Yanzu haka dai an sanya jami’an tsaro da suka hada har da sojoji da yawansu ya kai dubu 20 a cikin shirin ko ta-kwana a birnin na Bangkok.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu