An kashe mutane hudu a Kudancin Thailand
Wasu mutane dauke da makamai sun kashe wasu mutanen karkara su hudu a Gundumar Nongchik yayin da kasar ke fuskantar barazana daga masu zanga zangar siyasa.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce kisan na da alaka da masu ta da kayar baya a a kasar yayin da a yanzu haka ana neman wani mutum na biyar dab a san inda yake ba.
Fiey da mutane 5000 sun mutu tun daga shekarar 2004 a kudancin kasar dake da rinjayen Musulmi inda harkar tsaro ta tabarbare duk matakan sasantawar da aka dauka a baya.
Masana siyasar kasar sun ce akwai sauran tafiya a game da samar da zaman lafiya a kasar ganin cewa hukumomin kasar na jan kafa wajen biyan bukatun ‘yan tawayen da suka nema.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu