Isa ga babban shafi
Thailand

‘Yan bindiga sun budewa gangamin ‘Yan adawa wuta a Thailand

Wasu ‘Yan bindiga sun bude wa gangamin ‘Yan adawa wuta a kasar Thailand wanda ya kara hura wutar rikicin kasar inda ake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Firaminista Yingluck Shinawatra. Rahotanni sun ce mutum guda ya mutu wasu da dama kuma sun samu rauni.

Gungun masu zanga-zangar kin jinin gwamnati a kasar Thailand
Gungun masu zanga-zangar kin jinin gwamnati a kasar Thailand
Talla

Masu zanga zangar da suka yi sansani a kusa da cibiyar gwamnati a birnin Bangkok na kasar Thailand a daren Juma’a zuwa safiyar Assabar sun fuskanci harbin bindiga da ya yi sanadiyar mutuwar mutum guda kamar yadda jami’an kai dauki suka tabbatar

Wadanda suka bayyana cewa, wasu mutanen 3 da suka jikkata a sakamakon harbin an kwantar da su a asibiti

Wannan hari ya zo ne kwanaki biyu da faruwar tashin hankalin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 2 da suka hada da Dan sanda guda da wani mai zanga zanga, a yayinda wasu 150 suka jikkata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.