Isa ga babban shafi
China

Kotun China ta yi watsi da daukaka karar Xilai

Wata Kotun daukaka kara a kasar China, taki amincewa da daukaka karar da fitaccen Dan siyasar kasar Bo Xilai ya yi kan hukuncin daurin rai da rai da aka masa, bayan samunsa da laifin cin hanci da almubazzaranci da kuma amfani da ofishinsa ta hanyar da bata kamata ba.

Bo Xilai, a gaban kotun China
Bo Xilai, a gaban kotun China AFP PHOTO / CCTV
Talla

Wannan hukunci da kotun Shandong ta yanke, ya kawo karshen duk wata fafutuka na sauya hukuncin da Bo Xilai ke bukata, na ganin ya wanke kansa daga tuhume tuhumen da aka masa na cin hanci da rashawa.

Kafin shekarar 2012, Bo Xilai na daga cikin manyan ‘Yan siyasar China kuma shugaban birnin Chongqing, da ke kudu maso Yammacin kasar.

Wannan hukunci, ya kawo karshen siyasar Bo Xilai, kamar yadda lauyansa ya bayyana, kuma yana da wuya a sake ganin sa a bainar jama’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.