Isa ga babban shafi
Isra'ila-Felesdinu

Isra’ila ba ta da hurumin yin adawa da daga darajar Falasdinawa- Olmert

Tsohon Firaministan Isra’ila, Ehud Olmert, yace ba su da hurumin kin amincewa da daga darajar kasar Falasdinu a matsayin ‘Yar kallo a zauren Majalisar Dinkin Duniya. Ya kuma ce gina sabbin gidaje a yankunan Falasdinawa bai dace ba.

Tsohon Shugaban Masar'Hosni Moubarak da Tsohon shugaban Falasdinawa Yasser Arafat da tsohon Firaministan Isra'ila Ehud Barak a wani taron sasana rikicin Isra'ila da Falasdinawa da Masar ke shiga tsakani
Tsohon Shugaban Masar'Hosni Moubarak da Tsohon shugaban Falasdinawa Yasser Arafat da tsohon Firaministan Isra'ila Ehud Barak a wani taron sasana rikicin Isra'ila da Falasdinawa da Masar ke shiga tsakani Reuters
Talla

Olmert wanda ake saran zai bayyana shirinsa na shiga takarar zabe mai zuwa, yace shirin Isra’ila na gina sabbin gidaje a Yankunan Falasdinawa bai dace ba, yana mai cewa lokaci na kurewa na tattaunawa da Falasdinawa domin samun dawamammen zaman lafiya.

A ranar 29 ga watan Nuwamba ne Falasdinawa suka samu nasarar samun kujerar 'Yan kallo a zauren Majalisar Dinkin duniya bayan kwashe shekaru suna gwagwarmaya duk da adawar Isra'ila da Amurka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.