Ana zargin sojojin Burkina Faso da amfani da jiragen yaki marasa matuka kan fararen hula- HRW
Rahoton da kungiyar mai zaman kanta ta Human Rights Watch ta (HRW) ta fitar wanda aka buga ranar Alhamis 25 ga watan Janairu, 2024,na bayyana cewa akalla fararen hula 60 ne aka kashe a hare-haren soji da sunan yaki da da mayakan jihadi.
Wallafawa ranar:
Tsakanin Agusta da Nuwamba 2023, hare-hare ta sama guda uku dakarun Burkina Faso suka kai Bouro, Bidi da Boulkessi, a arewacin kasar.
Wadanan hare-hare sun haifar da barna a kasuwanni da wuraren bikin da jana'iza. Sai dai a cewar shedun da kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Human Rights Watch ta tattara, wadanda abin ya shafa ba ’yan ta’adda ba ne.
Bayan wadannan kalaman, marubucin rahoton, mai bincike IIaria Allegrozzi, da Frédéric Garat daga Rfi ya yi hira da ita, ta nuna rashin jin dadin yadda al'ummar duniya gaba daya ke nuna rashin jin dadin abin da ke faruwa a wannan kasa ta Burkina Faso.
labarai."
Kungiyar ta HRW ta na mai ga kasashen Duniya na ganin sun mayar da hankali ga kasar ta Burkina Faso tare da jan hankali majalisar Sojin kasar na ganin ta kawo karshen wannan barna saman farraren hula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu