Isa ga babban shafi

Guguwar Belal ta haddasa ambaliyar ruwa a sassan Maurituis

Ambaliyar ruwa ta afka wa wasu sassan Mauritius sakamakon kakkarfar guguwar da ta isa kasar da ta kasance tsibiri a wani bangaren tekun India.

Yadda guguwar Belal ta afka wa sassan Port Louis, babban birnin kasar Mauritius.
Yadda guguwar Belal ta afka wa sassan Port Louis, babban birnin kasar Mauritius. AFP - RICHARD BOUHET
Talla

Hotunan da aka yada ta kafafen sada zumunta sun nuna yadda motoci masu yawan da ke kan manyan hanyoyin Port Louis babban birnin kasar ta Maurituis suka nutse a ambaliyar ruwan, yayin da kuma ruwan laka hade tarin shara ya mamaye unguwannin birnin a daidai  lokacin da ruwan sama kamar da bakin kwarya ke ci gaba  da shatata.

Mahukuntan Maurituis din sun ce ya zuwa lokacin wannan wallafa mutum guda ne ya rasa ransa, tare da gargadin cewa adadin ka iya karuwa sakamakon guguwar Belal da ta akfa musu cikin tsala karfin gudun da ya kai na kilomita 130 a sa’a guda.

Kididdiga ta nuna cewar sal goma zuwa sha biyu  kakkarfar guguwa  ke afka wa sassan Mauritius a duk shekara a tsakanin Afrilun zuwa Nuwamba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.