Isa ga babban shafi

Majalisar Dinkin Duniya na neman kudade don magance matsalar 'yan gudun hijira a duniya

Wasu alkaluma da ake da su na bayyana cewa duk  da girman rikicin Gaza, bai kamata kasashen duniya su manta da dubun-dubatar ‘yan gudun hijira a duniya ba, kalaman Shugaban hukumar ‘yan gudun hijira, Filippo Grandi, a wajen bude taron kolin ‘yan gudun hijira na duniya, wanda ke gudana har zuwa ranar 15 ga watan Disamba na wannan shekara  a Geneva.

Wasu 'yan gudun hijira a Maiduguri, wadanda rikicin Boko Haram ya raba da muhallansu a jihar Borno.
Wasu 'yan gudun hijira a Maiduguri, wadanda rikicin Boko Haram ya raba da muhallansu a jihar Borno. © REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Shugaban hukumar ‘yan gudun hijira, Filippo Grandi ya bayyana damuwa matuka," ,ya kuma bayyana cewa, ya zama wajibi hukumar ta sallami kusan mukamai 900 daga cikin 20,000.

Ya zuwa wannan lokaci kungiyar ta na bukatar dala miliyan 400 kusan (Euro miliyan 371) nan da karshen shekara.

Yaki a Ukraine, tashe-tashen hankula a Sudan, Habasha, rikicin jin kai a Afghanistan,hukumar ta fitar da wasu alkaluma inda ta ke cewa sama da mutane miliyan 114 ne suka rasa matsugunansu a fadin duniya a karshen watan Satumba.

Sansanin 'yan gudun hijira mafi girma a duniya kenan da ke kasar Kenya
Sansanin 'yan gudun hijira mafi girma a duniya kenan da ke kasar Kenya © UNHRC

Rahoto daga Hukumar na nuni yawan ‘yan gudun hijira a duniya ya ninka a cikin shekaru bakwai da suka gabata, inda ya kai mutane miliyan 36.4 a tsakiyar shekarar 2023.

Shugaban hukumar ya tabbatar da cewa "babban bala'in bil'adama na faruwa a zirin Gaza", kuma ya yi hasashen "karin mutuwa da wahala a tsakanin fararen hula, da kuma kara yawan yan gudun hijirar daga yankin.

Dubban mutane ne suka tsere daga wani sansanin 'yan gudun hijira da ke kusa da Kibumba, mai tazarar kilomita 40 daga arewacin Goma a gabashin Kongo, Litinin, 27 ga Oktoba, 2008. Dubban 'yan gudun hijira da sojoji ne ke tserewa fadan da ake yi a gabashin Kongo a wani abin da ake ganin kamar ya zama ruwan dare. babban ja da baya na dakarun gwamnati da 'yan tawayen Janar Laurent Nkunda suka kai wa hari. (Hotunan AP/Karel Prinsloo)
Dubban mutane ne suka tsere daga wani sansanin 'yan gudun hijira da ke kusa da Kibumba, mai tazarar kilomita 40 daga arewacin Goma a gabashin Kongo, Litinin, 27 ga Oktoba, 2008. Dubban 'yan gudun hijira da sojoji ne ke tserewa fadan da ake yi a gabashin Kongo a wani abin da ake ganin kamar ya zama ruwan dare. babban ja da baya na dakarun gwamnati da 'yan tawayen Janar Laurent Nkunda suka kai wa hari. (Hotunan AP/Karel Prinsloo) AP - KAREL PRINSLOO

Sai dai jami'in ya saba sukar kasashen da a idonsa ba sa bude kofofinsu ga 'yan gudun hijira.

Ya sake yin nuni da cewa a ranar Laraba shirin gwamnatin Burtaniya na mai da hankali kan korar bakin haure da suka isa Birtaniya ba bisa ka'ida ba zuwa kasar Rwanda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.