Isa ga babban shafi

WFP na shirin katse tallafin abinci ga ‘yan gudun hijira sama da miliyan 1 a Chadi

Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP) ta ce a watan Janairu za ta kawo karshen tallafin abinci ga kimanin ‘yan gudun hijara miliyan 1.4 a kasar Chadi da suka hada da sabbin zuwa da suka tsere daga tashin hankali a yankin Darfur na kasar Sudan saboda karancin kudi.

Wasu 'yan gudun hijarar Sudan da ke neman mafaka a Chadi
Wasu 'yan gudun hijarar Sudan da ke neman mafaka a Chadi © Zohra Bensembra / Reuters
Talla

WFP ta kara da cewa matsalar kudi da karuwar bukatun jin kai sun tilastawa hukumar dakatar da bayar da agaji ga ‘yan gudun hijira da masu neman mafaka a cikin gida daga Najeriya da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da Kamaru daga watan Disamba.

Hukumar ta ce daga watan Janairu, dakatarwar zai shafi a ‘yan gudun hijira da ke cikin mawuyacin hali a Chadi, in ji WFP a ranar Talata a cikin wata sanarwa.

Fiye da 'yan gudun hijira 540,000 ne suka tsallaka daga Sudan zuwa kasar Chadi tun bayan yakin da ya barke watanni 7 da suka gabata tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF a cewar kungiyar kula da 'yan cirani ta duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.