Isa ga babban shafi

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin barkewar cututtuka a Libya

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa birnin Derna, wanda ya fuskanci matsalar ambaliya, inda dubban mutane suka mutu mako guda da ya wuce  yana fuskantar barazanar barkewar cututtuka da za ta iya haifar da wata matsala mai tayar da hankali.

Magatakardan Majalisar Dinkin Duniyal Antonio Guterres.
Magatakardan Majalisar Dinkin Duniyal Antonio Guterres. AP - Khalil Senosi
Talla

Mummunar ambaliyar da ta yi sanadin mutuwar mutane sama da dubu 3, da bacewar dubbai ta zo ne a lokacin a kasar, wanda ke arewacin nahiyar Afirka ta fuskanci mummunar barna daga mahaukaciyar guguwar Daniel.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce al’ummar yankin sama da dubu 30 ne ke matukar bukatar tsaftataccen ruwan sha da sauran mahimman kayayyaki, a yayin da suke dada nutsewa cikin hadarin kamuwa da cutuka da suka hada da kwalara, amai da gudawa, karancin abinci mai gina jiki da sauran su.

Kwamitin da Majalisar Dinkin Duniya  ta aike Libya don taimaka wa wadanda mahaukaciyar guguwar Daniel da kuma ambaliya suka yi wa ta’adi su na  ta aikin bada agaji ba kakkautawa.

Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da suka hada da Asusun tallafa wa Yara na UNICEF, Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira  da Hukumar Samar da Abinci sun kasance a cikin birnin Derna su na taimaka wa wadanda suka tsira daga iftila’in da ya afka wa birnin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.