Isa ga babban shafi

Kotun ICC ta kaddamar da bincike kan kashe-kashen yakin Darfur

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa na gudanar da bincike kan tashe-tashen hankula a yankin Darfur na kasar Sudan. Cikin wannan bincike har da rahotannin kashe-kashe da fyade da kuma laifukan da suka shafi kananan yara, kamar yadda babban mai gabatar da kara ya shaida wa Majalisar Dinkin Duniya a ranar alhamis.

Wasu mazauna yankin Darfur da rikici ya raba da gidajensu, yayin da suke isa sansanin 'yan gudun hijira na Zamzam dake arewacin Darfur.
Wasu mazauna yankin Darfur da rikici ya raba da gidajensu, yayin da suke isa sansanin 'yan gudun hijira na Zamzam dake arewacin Darfur. ASSOCIATED PRESS - Sarah El Deeb
Talla

Dakarun dake fada da juna na ci gaba da fafatawa a babban birnin kasar Khartoum da kuma wasu yankunan kasar Sudan a rikicin da ya barke a tsakiyar watan Afrilun shekarar nan.

Wasu mata da rikici ya raba da muhallansu a wani sansanin 'yan gudun hijira dake yankin Darfur.
Wasu mata da rikici ya raba da muhallansu a wani sansanin 'yan gudun hijira dake yankin Darfur. ASSOCIATED PRESS - Nasser Nasser

Fiye da mutane miliyan 3 ne suka rasa muhalan su, inda da fiye da 700,000 da suka yi hijira zuwa kasashe makwabta.Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya fada a makon da ya gabata cewa, Sudan, kasa ta uku mafi girma a Afirka, na gab da fuskantar yakin basasa da kan iya dagula zaman lafiya a yankin baki daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.